Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan bindiga Guddel da dan uwansa a wani samame da sojoji suka yi a jihar Kaduna.
An bayyana hakan ne a wani sako da wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine ya wallafa a shafin X.
An ce Guddel shi ne ke da alhakin kai hare-hare da sace-sacen mutane da dama a sassan Kaduna da jihohin da ke makwabtaka da ita.
Bakatsine ya rubuta cewa: “Sojoji sun yi nasarar kawar da dan bindiga Guddel da dan uwansa a Kaduna.
A wani labarin makamancin haka, Bakatsine ya kuma ruwaito cewa rikicin da ya barke tsakanin ‘yan bindiga a garin Danmusa na jihar Katsina ya kai ga tserewa wasu da aka yi garkuwa da su daga Kankara.
Ya kara da cewa, “Rikicin da aka yi tsakanin ‘yan bindigar Danmusa ya taimaka wa wadanda aka yi garkuwa da su daga Kankara su tsere, an kashe ‘yan bindiga da dama, ciki har da wani babban shugaba a rikicin,” in ji shi.
Har ya zuwa lokacin wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da lamarin ba.