fidelitybank

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Date:

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan bindiga Guddel da dan uwansa a wani samame da sojoji suka yi a jihar Kaduna.

An bayyana hakan ne a wani sako da wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine ya wallafa a shafin X.

An ce Guddel shi ne ke da alhakin kai hare-hare da sace-sacen mutane da dama a sassan Kaduna da jihohin da ke makwabtaka da ita.

Bakatsine ya rubuta cewa: “Sojoji sun yi nasarar kawar da dan bindiga Guddel da dan uwansa a Kaduna.

A wani labarin makamancin haka, Bakatsine ya kuma ruwaito cewa rikicin da ya barke tsakanin ‘yan bindiga a garin Danmusa na jihar Katsina ya kai ga tserewa wasu da aka yi garkuwa da su daga Kankara.

Ya kara da cewa, “Rikicin da aka yi tsakanin ‘yan bindigar Danmusa ya taimaka wa wadanda aka yi garkuwa da su daga Kankara su tsere, an kashe ‘yan bindiga da dama, ciki har da wani babban shugaba a rikicin,” in ji shi.

Har ya zuwa lokacin wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da lamarin ba.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp