fidelitybank

Sojoji sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram a Borno

Date:

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce, sojojinta masu aiki ƙarƙashin shirin ‘Operation Hadin Kai’ da ke yaƙi da ayyukan masu tayar da ƙayar baya sun kashe manyan kwamandojin Boko Haram a hare-hare ta sama da suka kai a a ranar 16 ga wannan wata na Agusta a jihar Borno.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da rundunar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta AVM Edward Gabkwet a yau Laraba.

Sanarwar ta ce “rundunar ta kai harin ne kan ƴan ta’addan da suka yi hijira zuwa yankin daga wasu wurare da ke kusa”.

“Hare-haren sojojin ta sama sun yi nasarar halaka ƴan ta’adda da dama da suka hada da manyan kwamandojinsu biyar da kuma yaransu 35 tare da lalata maɓoyarsu da kayan aikinsu.

“Bayanai masu ƙarfi da aka tattara sun nuna cewa manyan ƴan ta’adda da ke a wurin da aka kai harin a daidai lokacin sun haɗa da Munzir Arika, Sani Dilla (Dan Hausawan Jubillaram), Ameer Modu, Dan Fulani Fari Fari, da Bakoura Arina Chiki, sai kuma sauran wasu ƴan bindiga 35.”

Sanarwar ta ce “Ana sa ran nasarar kashe waɗannan kwamandojin da mayakansu zai rage ƙarfin wadannan kungiyoyi ƴan ta’adda na ƙara kai hare-hare ko sake haɗuwa a yankin.”

Najeriya na yaƙi da mayaƙan ƙungiyar Boko Haram tsawon sama da shekaru 10 da suka gabata, rikicin da ya yi sanadin mutuwar dubban al’umma da kuma tarwatsa sama da mutum miliyan ɗaya daga gidajensu.

Duk da cewa gwamnatin Najeriya ta yi iƙirarin karya lagon mayaƙan, amma har yanzu akan samu hare-hare nan da can a yankin na arewa maso gabashin ƙasar.

A ƙarshen watan Yuli, wasu mayaƙa da ake zargin ƴan Boko Haram ne sun kai hari a jihar ta Borno wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 16.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp