Dakarun hadin gwiwa na kasa da kasa (MNJTF) sun kashe kwamandojin Boko Haram 10 da kungiyar IS da ke Yammacin Afirka (ISWAP) da kuma ‘yan ta’adda sama da 100 a wani samame na kasa da na sama a yankin tafkin Chadi.
Wannan farmakin mai suna Operation Lake Sanity na hadin gwiwa ne tare da hadin gwiwar dakarun MNJTF daga Najeriya, Nijar, da Kamaru da sojojin Operation Hadin Kai (OPHK- Nigeria) da kuma sojojin sama na MNJTF da OPHK da sauran hukumomin tsaro da kuma Civilian Joint Taskforce (CJTF).
A cewar sanarwar da kakakin rundunar ta MNJTF, Kanar Muhammad Dole, ya ce, wasu daga cikin yankunan da sojojin suka fatattake sun hada da Zanari, Arina Woje wanda ya kasance wani babban taron bita na kirkire-kirkire ga ‘yan ta’addan.
Sauran yankunan sun hada da Asagar, Larki, Garere, Kerenoa, Wurje, Arege, Abadam, Doron Lelewa, Kolaram, da sauran wurare da dama da ke kewaye da tsibiran.
Sai dai sojoji 18 sun samu raunuka yayin da wasu uku da kuma wani jami’in CJTF suka mutu a yayin samamen.
Dole, ya ce, an kashe ‘yan ta’addan da kwamandojinsu a tsawon lokacin da aka kai farmakin, biyo bayan hare-haren da rundunar hadin gwiwa ta sama da ta kai ta sama a tsibirin tafkin Chadi da bayanan sirri suka yi.
Ya lissafa wasu kwamandojin da aka kashe sun hada da Abubakar Dan Buduma, Abubakar Shuwa, Abu Ali, da Abu Jubril