fidelitybank

Sojoji sun kashe kasurgumin dan fashin daji a Neja

Date:

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce ta samu nasara halaka wasu ‘yan bingida a jihar Naija ciki har da wani gawurtaccen ɗan bindiga da ya jima yana addabar jama’a, mai suna Yellow Jambros.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fita mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labaranta, Air Commodore Edward Gabkwet, ta ce ‘yan bindigar sun gamu da ajalisun ne a ranar Laraba 6 ga watan Disamba a gundumar Galadima Kogo, a daidai lokacin da suke yunƙurin tsallaka kogi zuwa yankin Wurukuvhi na ƙaramar hukumar Chikun a jihar Kaduna mai makwabtaka.

Kafin kisan nasu, an yi ta bin diddigin Yellow Jambros, tare da mabiyansa waɗanda suka taso daga jihar Zamfara a kan babura 13 inda suka nufi Kusasu na ƙaramar hukumar Shiroro a jihar Naija.

Sanarwar ta ce da suka isa Kusasu, wasu ƙarin babura biyar sun shiga tawagar tasu, inda suka zama babura 18, daga nan kuma suka nufi kogin Jikudna.

”Da isarsu kogin ne ‘yan bindigar suka hau kwale-kale tare da baburansu 18 da nufin tsallakawa, suna tsaka da kogin ne kuma aka bayar da umarnin kai musu hari”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Air Commodore Edward Gabkwet ya ce an samu nasarar ƙaddamar da harin yadda aka tsara shi, inda aka kashe Yellow Jambros da sauran yaransa tare da lalata baburan da kuma nutsar da kwale-kwalen.

”Duk da cewa tafiyar ‘yan bindiga cikin ayari ba abu ne da aka saba gani ba, musamman da rana tsaka, Yellow Jambros tare da yaransa ba su yi tsammanin kai musu hari ta sama ba, saboda suna tunanin sojoji sun dakatar da kai hare-hare ta sama saboda da abin da ya faru na harin kuskure kan fararen hula a Tudun Biri, don haka suke son yin amfani da wannan damar”, in ji Edward Gabkwet.

Ya ƙara da cewa Yellow Jambros tare da yaransa sun sha ƙaddamar da hare-hare tare da yin garkuwa da mutane da kuma kashe su a kan babban titin Abuja zuwa Kaduna da kuma wasu garuruwa a jihohin Kaduna da Naija da Katsina da kuma Zamfara.

A watan Oktoban 2020 ‘yan sandan Zamfara suka kama wani gawurtaccen ɗan bindiga mai suna Mohammed Sani, wanda ya kashe fiye da mutum 50, saboda sun kasa haɗa masa kuɗin fansar da ya buƙata daga gare su.

A lokacin da ‘yan sandan ke tuhumarsa ya yi iƙirarin cewa shi yaron Yellow Jambros ne, wanda ke samar masa da jabun tufafin sojoji da na ‘yan sanda da bindigogi da sauran makaman da yake buƙata. In ji BBC.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp