fidelitybank

Sojoji sun kashe ɗan fashin dajin Bauchi

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe dan fashi guda a wani ƙwanton-ɓauna da sojojin suka yi wa tawagar ‘yan fashin a yankin Bura na ƙaramar hukumar Ningi da ke jihar Bauchi.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Asabar, mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Burgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya ce sojojin sun amfani da bayanan sirri da suka samu game da ‘yan fashin.

“Sojojin sun yi wa ‘yan fashin kwanton-ɓauna tare da buɗe musu wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwar guda daga cikinsu, yayin da sauran suka tsere da raunukan harbin bingiga a jikinsu”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sojojin sun kuma ce sun samu nasarar ƙwato bindiga guda ƙirar Ak-47 da alburusai 14, da wayar hannu da kuma guru da layu daga ɗan fashin da suka kashe.

Sanarwar ta kuma ce sojojin na ci gaba da sintiri a yankin domin gano sauran ‘yan fashin da suka tsere.

Yankin arewa maso yammacin Najeriya ne dai ya fi fama da matsalar ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane, to sai dai a baya-bayan matsalar ta fara ɓulla a wasu yankunan jihar Bauchi da ke kudu maso gabashin ƙasar.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp