Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe dan fashi guda a wani ƙwanton-ɓauna da sojojin suka yi wa tawagar ‘yan fashin a yankin Bura na ƙaramar hukumar Ningi da ke jihar Bauchi.
Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Asabar, mai ɗauke da sa hannun jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Burgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya ce sojojin sun amfani da bayanan sirri da suka samu game da ‘yan fashin.
“Sojojin sun yi wa ‘yan fashin kwanton-ɓauna tare da buɗe musu wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwar guda daga cikinsu, yayin da sauran suka tsere da raunukan harbin bingiga a jikinsu”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.
Sojojin sun kuma ce sun samu nasarar ƙwato bindiga guda ƙirar Ak-47 da alburusai 14, da wayar hannu da kuma guru da layu daga ɗan fashin da suka kashe.
Sanarwar ta kuma ce sojojin na ci gaba da sintiri a yankin domin gano sauran ‘yan fashin da suka tsere.
Yankin arewa maso yammacin Najeriya ne dai ya fi fama da matsalar ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane, to sai dai a baya-bayan matsalar ta fara ɓulla a wasu yankunan jihar Bauchi da ke kudu maso gabashin ƙasar.