fidelitybank

Sojoji sun kashe ƴan bindiga 22 a Katsina

Date:

Rundunar sojin sama ta Najeriya, ta kashe akalla ‘yan bindiga 22 a ƙananan hukumomin Jibiya da Batsari a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin ƙasar.

Jaridar PRNigeria ta ruwaito ce wa ‘yan bindigar – waɗanda galibinsu yaran riƙaƙƙen ɗan bindigar nan ne da aka kashe Abdulkareem Boss – an kashe su ne ranar Litinin, a wani hari ta sama da dakarun rundunar ‘Hadarin Daji’ mai yaki da ‘yan bindiga – a yankin arewa maso yammacin ƙasar – ta kai.

Wata majiya mai ƙarfi a rundunar sojin ta shaida wa PRNigeria cewa an kai harin ne a kan tsaunukan da ‘yan bindigar ke ɓoye, bayan samun bayan sirri da ke nuna cewa suna kitsa wani hari domin yin garkuwa da matafiya a kan hanyar Jibiya zuwa Katsina.

Majiyar ta ce ‘yan bindigar sun addabi al’umomin yankin, inda suke yin garkuwa da mazaunan wasu yankuna a ƙaramar hukumar Kankara.

Harin wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindiga da dama , ya kuma lalata sansanonin ‘yan bindigar.

A cikin watan Agustan 2022 ne dai rundunar sojin sama ta Najeriya ta kashe fitaccen ɗan bindigar nan mai suna Abdulkareem Boss tare da wasu daga cikin yaransa a wani hari ta sama da rundunar ta ƙaddamar kan maɓoyarsu a dajin Ruga da ke jihar Katsina.

An zargi Abdulkareem da kitsi wani mummunan hari da ya yi sanadin kashe wani babban baturen ‘yan sanda a ƙaramar hukumar Dutsinma ranar 5 ga watan Yulin 2022.

Mai maganar da yawun rundunar sojin sama ta Najeriya Air Commodore Edward Gabkwet, wanda ya tabbatar da harin na ranar Litinin, ya ce babban hafsan sojin sama na ƙasar, Air Vice Marshal Hasan Abubakar, ya umarci dakarun sojin saman ƙasar da su haɗa kai da sauran jami’an tsaro domin kakkafe duka ‘yan ta’addan da kuma maɓoyarsu

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp