fidelitybank

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Date:

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar Chana, bisa zarginsa da hannu wajen kai wa ’yan ta’adda kayayyaki a jihar Borno.

Daraktan Yada Labaran Shalkwatar Tsaron Ƙasar nan Manjo Janar Markus Kangye ne, ya bayyana hakan ranar Juma’a a Abuja, yayin ganawa da manema labarai.

Ya ce, an kama mutumin ne a wani samame da sojoji suka gudanar a kananan hukumomin Kukawa da Ngala da ke jihar Borno, inda ake zargin yana fakewa da aikin hakar ma’adanai.

Kangye ya ce yanzu haka an tsare dan Chanan, kuma ana masa tambayoyi domin gano hakikanin abinda ya kai shi yankin da kuma yiwuwar ko akwai wasu da ke tare da shi.

Ya kara da cewa bayan kammala bincike, za a bayyana wa jama’a cikakken bayani kan abin da ya faru, da matsayin da wanda ake zargin ke ciki.

Sojojin sun kuma sanar da cewa daruruwan ’yan Boko Haram da ISWAP sun mika wuya daga ranar 6 zuwa 11 ga Yuni, sakamakon yadda suka tsananta ayyukan tsaro a yankin arewa maso gabas.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp