Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar Chana, bisa zarginsa da hannu wajen kai wa ’yan ta’adda kayayyaki a jihar Borno.
Daraktan Yada Labaran Shalkwatar Tsaron Ƙasar nan Manjo Janar Markus Kangye ne, ya bayyana hakan ranar Juma’a a Abuja, yayin ganawa da manema labarai.
Ya ce, an kama mutumin ne a wani samame da sojoji suka gudanar a kananan hukumomin Kukawa da Ngala da ke jihar Borno, inda ake zargin yana fakewa da aikin hakar ma’adanai.
Kangye ya ce yanzu haka an tsare dan Chanan, kuma ana masa tambayoyi domin gano hakikanin abinda ya kai shi yankin da kuma yiwuwar ko akwai wasu da ke tare da shi.
Ya kara da cewa bayan kammala bincike, za a bayyana wa jama’a cikakken bayani kan abin da ya faru, da matsayin da wanda ake zargin ke ciki.
Sojojin sun kuma sanar da cewa daruruwan ’yan Boko Haram da ISWAP sun mika wuya daga ranar 6 zuwa 11 ga Yuni, sakamakon yadda suka tsananta ayyukan tsaro a yankin arewa maso gabas.