Dakarun rundunar sojojin Najeriya, sun kashe wasu mayakan kungiyar ta’addanci na Boko Haram.
Daraktan yada labarai na ayyukan tsaro, Manjo Janar Bernard Onyeuko ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis, 10 ga watan Fabrairu, a taron manema labarai.
Ya ce, dakarun sun kuma kama ‘yan ta’adda 50, sannan suka kwato motocin harbi guda 5, makamai iri-iri guda 50 da kuma alburasai daban-daban guda 200 daga yan ta’addan.
Hakazalika, jimlar yan ta’adda 965 da iyalansu da yara 550 ne suka mika wuya ga dakarun da aka tura wurare mabanbanta da suka hada da Gamboru, Tumbumma, Kukawa, Baga, Gwoza, Mallam Fotori, Damboa, Kirta Wulgo, Bun Yadi, Gujiba, Madiya duk a jihohin Borno da Yobe.