fidelitybank

Sojoji sun kama shugaban PDP na mazaba a Zamfara da tallafawa ‘yan bindiga

Date:

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Hadarin (OPHD) sun kama wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a jihar Zamfara.

Daya daga cikin wadanda ake zargin, Aminu Ibrahim, ana zarginsa da kasancewa shugaban jam’iyyar PDP, shugaban gundumar Birnin Yero a karamar hukumar Shinkafi a jihar.

Wata majiyar leken asiri ta soji a jihar ta ce an kama Ibrahim, tare da abokan sa da aka fi sani da Musa Usman Seun da Isah Mohammed ranar Litinin.

Majiyar ta ci gaba da cewa: “Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Haderin Daji sun yi aiki da sahihan bayanan sirri kan ayyukan wani dan bindiga da ya yi yunkurin shigo da makamai cikin jihar.

Wannan kafar yada labarai ta kuma samu labarin cewa sojojin sun yi gaggawar tare hanya inda suka kame mutanen uku da ake zargin ‘yan bindiga ne.

“Wadanda ake zargin su 3, Musa Usman Seun, Aminu Ibrahim, da Isah Mohammed, an kama su ne a Shinkafi a ranar 22 ga watan Janairun 2024, kuma an kama su da kudi naira miliyan biyu da dubu dari biyar da tamanin, Volkswagen Wagon 1, wayoyin hannu 3 da sauran kayayyaki.

“Bincike na farko ya nuna cewa makudan kudaden da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin na musayar muggan makamai ne a kan iyakar Illela a jihar Sakkwato. Ana ci gaba da yi wa wadanda ake zargin tambayoyi.”

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp