Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Hadarin (OPHD) sun kama wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne a jihar Zamfara.
Daya daga cikin wadanda ake zargin, Aminu Ibrahim, ana zarginsa da kasancewa shugaban jam’iyyar PDP, shugaban gundumar Birnin Yero a karamar hukumar Shinkafi a jihar.
Wata majiyar leken asiri ta soji a jihar ta ce an kama Ibrahim, tare da abokan sa da aka fi sani da Musa Usman Seun da Isah Mohammed ranar Litinin.
Majiyar ta ci gaba da cewa: “Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Haderin Daji sun yi aiki da sahihan bayanan sirri kan ayyukan wani dan bindiga da ya yi yunkurin shigo da makamai cikin jihar.
Wannan kafar yada labarai ta kuma samu labarin cewa sojojin sun yi gaggawar tare hanya inda suka kame mutanen uku da ake zargin ‘yan bindiga ne.
“Wadanda ake zargin su 3, Musa Usman Seun, Aminu Ibrahim, da Isah Mohammed, an kama su ne a Shinkafi a ranar 22 ga watan Janairun 2024, kuma an kama su da kudi naira miliyan biyu da dubu dari biyar da tamanin, Volkswagen Wagon 1, wayoyin hannu 3 da sauran kayayyaki.
“Bincike na farko ya nuna cewa makudan kudaden da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin na musayar muggan makamai ne a kan iyakar Illela a jihar Sakkwato. Ana ci gaba da yi wa wadanda ake zargin tambayoyi.”