fidelitybank

Sojoji sun kama mai hada-hadar bindiga a Taraba

Date:

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta tare da hadin gwiwar ‘yan banga sun cafke wani da ake zargin dan bindiga ne a Taraba.

Wanda ake zargin, Mansir Mohammed, an kama shi ne a tashar mota ta Jalingo bisa zarginsa da bayar da makamai ga ‘yan ta’adda.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Maj.-Gen. Onyema Nwachukwu, ranar Litinin a Abuja.

Nwachukwu ya ce sojojin sun kuma dakile yunkurin yin garkuwa da su tare da kawar da wani dan ta’adda a yayin samamen.

Ya ce kama Mohammed ya kai ga kama wasu mambobin kungiyarsa tare da kwato bindigar Semi-Automatic Pump Action guda daya.

Ya ce sauran kayayyakin da aka kwato sun hada da bindiga guda daya, mota kirar Peugeot, wayoyin hannu guda biyar, da kudi N45,000.

Nwachukwu ya ce sojojin sun yi wani samame na daban a kauyen Miyande da ke karamar hukumar Takum a jihar, sun kama wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne guda biyu da suka boye bindigogi masu sarrafa kansu a karkashin kujerar babur.

Ya kara da cewa an kwato bindiga kirar AK- 47 guda 5, harsashi na musamman mai girman 7.62mm da kuma babur a hannun su.

“A wani labarin kuma, sojojin sun amsa kiran da aka yi musu na nuna bacin rai, inda suka yi nasarar dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a garin Zaki-Biam da ke karamar hukumar Zaki-Biam a jihar Benue.

“A yayin shiga tsakani, sojoji sun kashe wani mai garkuwa da mutane a wata musayar wuta da masu laifin tare da kwato bindigar Beretta tare da harsashi hudu na tara.

“Wadannan ayyuka da suka samu nasara suna nuna jajircewar rundunar sojin Najeriya wajen kawar da ta’addanci da tada kayar baya a yunkurinta na tabbatar da tsaro a kasar.

“Muna kira ga jama’a da su ci gaba da ba sojojinmu goyon baya yayin da suke gudanar da ayyukansu,” in ji shi.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp