fidelitybank

Sojoji sun kama jirgin ruwa da gangar mai 3,665 na sata a Ondo

Date:

Rundunar sojin ruwa ta kasa, ta kama wani jirgin ruwa ɗauke da gangar mai 3,665 da take zargi na sata ne a yankin Igbokoda na jihar Ondo.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce ta kama ma’aikatan jirgin 17, da take zargi da satar man daga rijiyar mai ta Ebesan a ƙaramar hukumar Ilaje da ke jihar.

Daraktan yaɗa labaran rundunar, Commodore Ayo-Vaughan, ya ce an kama jirgin ne a ranar Alhamis.

Ya ce rundunar ta samu bayanan sirri kan ayyukan mutanen da take zargi da sace man, inda nan take ta tura jami’anta waɗanda suka yi nasarar kama mutanen.

Sanarwar ta ce sojojin sun gano cewa an daɗe ana amfani da jirgin wajen satar man daga kowane ɓangare na rijiyar.

Jirgin na da girman da zai iya ɗaukar nauyin metric ton 15,000, kuma a lokacin da aka kama shi yana ɗauke da man da nauyinsa ya kai metric ton 500.

Satar mai a kudancin Najeriya dai wata matsala ce da ta daɗe tana ci wa ƙasar tuwo a ƙwarya, inda ɓata-gari ke sace ɗimbin mai ta hanyar fasa bututan man ko amfani da rijiyoyin mai ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ke ƙara haifar da koma-baya kan tattalin arzikin ƙasar.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp