fidelitybank

Sojoji sun kai farmaki ga ‘yan Boko Haram a Borno

Date:

Dakarun sojojin Najeriya da aka tura yankin Arewa maso Gabas a ci gaba da kai farmakin da ‘yan ta’addan ke ci gaba da yi a ranar Juma’a, sun yi nasarar kai wani samame a sansanin ‘yan ta’adda da ke yankin Arra a dajin Sambisa, inda suka yi nasarar fatattakar ‘yan bindiga uku tare da lalata musu matsugunin su.

Major General Onyema Nwachukwu,
Daraktan hulda da jama’a na rundunar, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce sojojin sun kwato bindigogin AK-47 guda biyu da rigar kunar bakin wake.

“A wani farmakin da sojojin suka kai a yankin Buluwa da ke karamar hukumar Kukawa a jihar Borno, inda suka gano tare da lalata wani sansanin ‘yan ta’addan,” in ji shi.

Ya ce yayin arangamar sojojin sun kashe dan ta’adda guda daya tare da kwato bindiga kirar AK-47 guda 14, 7.62mm (Special), keke, kayan abinci, injin nika, da sauran kayayyaki.

Ya ce rundunar sojin Najeriya ta dukufa wajen ganin ta kawar da ta’addanci da tada kayar baya a yankin, kuma za ta ci gaba da gudanar da ayyukan tabbatar da tsaro da tsaron jama’a.S

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp