fidelitybank

Sojoji sun ka farmaki Tafkin Chadi

Date:

Rundunar sojojin Najeriya tare da hadin gwiwar rundunonin sojojin hadin gwiwa da na Civilian Joint Task Force, sun yi nasarar kai farmaki a yankin tafkin Chadi da kungiyar Boko Haram/Islamic State West Africa Province, ISWAP.

A wata sanarwa da Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Maj.-Gen. Onyema Nwachukwu, a ranar Juma’a a Abuja, an gudanar da wannan farmakin ne a ranar Larabar da ta gabata tare da gwabza kazamin fada, inda aka kashe ‘yan ta’adda uku tare da kwato wata mota kirar Mine Resistant Ambush Protected, MRAP.

Sauran kayayyakin da aka kwato sun hada da wata babbar mota makare da bindigar kakkabo jirgin da tarin makamai da harsasai.

A cewar Nwachukwu, ‘yan ta’addan sun far wa sojojin ne da wata mota kirar Bama-bamai, VBIED, turmi, manyan bindigogi da kuma babura.

Ya ci gaba da cewa, ‘yan ta’addan sun fada karkashin babbar karfin wuta na sojojin, lamarin da ya tilasta musu barin sansaninsu da makamai da kayan aikinsu cikin rudani.

Wannan farmakin, a cewarsa, ya zama babban koma-baya ga ‘yan tada kayar bayan, yayin da dakarun da suka yi kaurin suna wajen fatattakar ‘yan ta’adda uku.

“Abubuwan da aka kwato sun hada da MRAP daya, motar bindiga daya, Bindigogin Dushka guda daya, Bindigogin AK 47 daya da kuma bindigar gida daya.

“Sojoji sun kuma kama Bam din Roket Propelled Grenade (RPG) guda daya, harsashi na musamman guda 273 na 7.62mm, na’urar Pumping guda daya, na’urorin Dushka 65, manyan bindigogi guda 48 da kuma babura guda uku.

“A yanzu haka dakarun soji suna amfani da nasarar da suka samu wajen fatattakar ‘yan ta’addan,” in ji shi.

Nwachukwu ya ce dakarun sojin Najeriya sun yi wani samame na daban a maboyar ‘yan ta’adda a kauyen Katakpa da ke karamar hukumar Toto a jihar Nasarawa, sun yi nasarar kawar da wani mai laifi guda daya.

Ya ce sojojin sun kuma kwato bindigogin AK-47 guda biyu, bindigu mai sarrafa kansa guda daya, mujallu AK-47 guda uku da harsashi na musamman 7.62 mm har guda 90.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp