fidelitybank

Sojoji sun harbe DPO ƴansanda a Zamfara

Date:

A wani yanayi mai kama da zaman tankiya tsakanin jami’an soji da na ƴansanda a ƙasar nan, wani soja ya harbe wani DPO na ’yansanda a jihar Zamfara.

Al’amarin dai ya faru ne a garin Ɗanmarke da ke karƙashin ƙaramar hukumar Bukkuyum ta jihar Zamfara a ranar Larabar nan da daddare, kamar yadda wata sanarwa da rundunar ƴansandan jihar ta Zamfara ta fitar.

SP Halliru Liman wanda shi ne DPO na Wasugu da ke jihar Kebbi ya gamu da ajalinsa ne a kan hanyarsa ta halartar taronsu na wata-wata, inda sojoji suka tsayar da shi a wani shingen bincike.

“Duk da cewa ya bayyana musu cewa shi ɗansanda kamar yadda suka buƙata amma kuma sai kawai wani soja mai suna Hassan ya zaro bindiga ya harbe SP Liman a kansa abin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.” In ji sanarwar.

Rundunar ƴansandan ta jihar Zamfara ta nemi da dukkan hukumomin da suke da ruwa da tsaki da su gudanar da cikakken bincike na yadda al’amarin ya faru.

“Abin da sojojin suka yi ya fito fili da irin rashin son aiki tare da sauran jami’an tsaro,” kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp