fidelitybank

Sojoji sun hallaka ƴan ISWAP 32

Date:

Jirgin yakin saman kasar nan ya kaddamar da hari ta sama mai, inda aka kai farmaki kan wani wurin taron mayakan kungiyar ISWAP da ke Dogon Chikun, Jihar Borno.

Rahotanni daga sahihan majiyoyi sun ce hare-haren sun kashe a kalla mayaka 32 na ISWAP, a harin da aka kai bayan rikici tsakanin bangarorin kungiyar.

Majiyoyin leken asiri sun bayyana wa Zagazola Makama, kwararren masani kan tsaro a yankin tafkin Chadi, cewa hare-haren sun lalata wurin da mayakan ISWAP suka sake haduwa bayan rikici da wata bangaren kungiyar.

Baya ga yawan mutanen da aka hallaka, an kuma lalata makamai da sauran kayayyaki masu mahimmanci na ‘yan ta’addan.

“An tsara wannan aiki a kan lokaci kuma an aiwatar da shi don rusa wurin taron kungiyar tare da rage karfinsu na kai hare-hare a nan gaba,” in ji wata majiya.

Operation Hadin Kai, aikin rundunar sojojin Najeriya don murkushe ta’addanci a Arewa maso Gabas, na ci gaba da kara kaimi wajen kai farmaki kan ISWAP da Boko Haram, tare da mayar da hankali kan wuraren boye da sansanonin kayan aiki.

Dogon Chikun, wanda aka san shi a matsayin wurin da ake yawan ayyukan ta’addanci, yana karkashin kulawar tsaro saboda muhimmancinsa ga ayyukan ISWAP.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp