fidelitybank

Sojoji sun hallaka ƴan ISWAP 32

Date:

Jirgin yakin saman kasar nan ya kaddamar da hari ta sama mai, inda aka kai farmaki kan wani wurin taron mayakan kungiyar ISWAP da ke Dogon Chikun, Jihar Borno.

Rahotanni daga sahihan majiyoyi sun ce hare-haren sun kashe a kalla mayaka 32 na ISWAP, a harin da aka kai bayan rikici tsakanin bangarorin kungiyar.

Majiyoyin leken asiri sun bayyana wa Zagazola Makama, kwararren masani kan tsaro a yankin tafkin Chadi, cewa hare-haren sun lalata wurin da mayakan ISWAP suka sake haduwa bayan rikici da wata bangaren kungiyar.

Baya ga yawan mutanen da aka hallaka, an kuma lalata makamai da sauran kayayyaki masu mahimmanci na ‘yan ta’addan.

“An tsara wannan aiki a kan lokaci kuma an aiwatar da shi don rusa wurin taron kungiyar tare da rage karfinsu na kai hare-hare a nan gaba,” in ji wata majiya.

Operation Hadin Kai, aikin rundunar sojojin Najeriya don murkushe ta’addanci a Arewa maso Gabas, na ci gaba da kara kaimi wajen kai farmaki kan ISWAP da Boko Haram, tare da mayar da hankali kan wuraren boye da sansanonin kayan aiki.

Dogon Chikun, wanda aka san shi a matsayin wurin da ake yawan ayyukan ta’addanci, yana karkashin kulawar tsaro saboda muhimmancinsa ga ayyukan ISWAP.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp