Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai sun ƙaddamar da hare-hare ta sama da ƙasa kan cibiyoyin ƴan Boko Haram da ISWAP da ke Nzalgana a ƙaramar hukumar Gujba da Timbuktu Triangle.
Wata sanarwa da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na X ta ce rundunar ta ce sakamakon hare-haren ya haifar da kisan ƴan ƙungiyar da jagororinsu da suka haɗa da Ameer Malam Jidda wanda babban kwamanda ne a ƙauyukan a Ngorgore da Malumti.
Bugu da ƙari, an samu ƙarin gawarwakin ƴan ta’adda sannan an ƙwato makamansu a wani hari da aka kai Malamfatori.
A baya-bayan nan dai ana ta samun ƙaruwar hare-haren Boko Haram da ISWAP, inda ko a watan da ya gabata sai da ƙungiyar ta kai wani harin jirgi maras matuƙi a garin Marte da ke jihar Borno.