fidelitybank

Sojoji sun Gano tarin makamai a Filato bayan da aka kashe wani Soja

Date:

Rundunar soji ta ce, dakarunta sun gano makamai masu yawa na zamani da kuma ƙirar gida a gundumar Fann da ke yankin ƙaramar hukumar Barikin Ladi a jihar Filato.

Cikin wata sanarwa da sojojin suka fitar sun ce sun ƙaddamar da samame a ƙauyukan gundumar ne bayan da wasu ɓata-gari suka kashe wani jami’in shige da fice a lokacin da jami’an tsaro ƙarƙashin rundunar Operation SAFE HAVEN ke sintiri a yankin.

An ce ɓata-garin sun kashe jami’in a lokacin da yake duba motarsu wadda aka yi zargin sun ɗauko makamai a cikinta.

Bayan haka ne jami’an sojojin suka ƙaddamar da samame da nufin gano makamai tare da kama mutanen da ake zargi da hannu a lamarin.

”Bayan shafe mako guda, dakarunmu sun kama mutum takwas tare da gano makamai na zamani da kirar gida a ƙauyukan Ratas da Ratoso da kuma Sangasa duka a gundumar Fann da ke yankin ƙaramar hukumar Barikin Ladi”, in ji sanarwar.

Makaman da aka gano a lokacin samamen sun haɗa da:

Bindiga ƙirar AK-47, 12 da samufurin AK-47 ƙirar gida 12, da ƙanannan bindigogi 15 da kwanson harsasan AK-47 15 da kakin soja, da harsasai 250 da sauran makamai da kwari da baka da babura bakwai.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp