Hedkwatar tsaron kasar nan ta ce, bataliyarta ta uku ta kama wasu gawurtattun ƴan fashin daji da suka addabi yankin arewa ta tsakiya.
Sanarwar da hedkwatar ta fitar, ta ce waɗanda aka kashe ɗin suna cikin wadanda aka jima ana nemansu ruwa a jallo.
Waɗanda aka kama ɗin sun haɗa da Bashir Mohammed da Ismail Mohammad, wadanda aka kama a jihar Filato tare da makamai bayan samun wani bayanan sirri daga jami’an tsaro.