fidelitybank

Sojoji sun fatattaki ‘yan bindiga a Kaduna

Date:

Rundunar soji ta tabbatar da kashe ƴan bindiga bakwai a Jihar Kaduna tare da ƙwato makamai.

Haka kuma wasu rahotannin na cewa sojojin sun daƙile wani hari da aka kai musu a wani sansanin su da ke Ƙaramar Hukumar Borgu ta Jihar Neja har sun kama kwamandan ƙungiyar ISWAP.

A wani saƙo da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na Facebbok, ta bayyana cewa tun da farko dakarun Operation Safe Forest Sanity ne suka ƙaddamar da wani samame a Maidaro da Tudun Kagi da Kusharki da kuma Anguwan Madaki duka da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari.

A yayin samamen, sojojin sun yi musayar wuta da ƴan bindigar inda suka kashe ƴan bindigar huɗu tare da ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da lodi biyu na harsasai samfarin 7.62mm da kuma bindiga ƙirar Pump Action ɗaya da harsasai uku da ƙananan bindigogi na gargajiya uku da babura huɗu.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp