Rundunar Sojin Najeriya, a ranar Asabar din da ta gabata, ta ce dakarun da ke karkashin runduna ta 6, sun lalata wani yanki na haramtacciyar kungiyar ‘yan asalin yankin Biafra, IPOB/Eastern Security Network, ESN, a garin Asaba na jihar Delta.
Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya ce farmakin da suka kai a ranar Asabar ya kai ga yin musayar wuta, lamarin da ya tilasta musu barin maboyarsu cikin rudani.
A sanarwar ya ce sojojin sun kama daya daga cikin mayakan da suka tsere tare da kwato bindigu kirar AK-47 guda biyar, Pump Action Semi Automatic rifles guda uku, bindiga G3 daya da kuma bindigar ganga guda daya.
Sauran kayayyakin da aka kwato sun hada da harsashi masu rai, injin lantarki, adduna, gatari da tutar kungiyar IPOB.
A cewarsa, sojojin sun lalata yankin tare da yin amfani da dajin wajen fatattakar mayakan da suka tsere.
Ya ce babban hafsan sojin kasa, Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya yabawa sojojin da sauran jami’an tsaro bisa kokarin da suke yi a ayyukan da suke ci gaba da yi, ya kuma bukace su da su ci gaba da dagewa don dawo da hayyacinsu a yankin.