fidelitybank

Sojoji sun daƙile harin Boko Haram a Borno

Date:

Rundunar sojin kasar nan ta ce, sojojinta na Operation Hadin Kai sun yi nasarar daƙile wani hari da ‘yan Boko Haram da /ISWAP suka kai da tsakar dare a garin Marte ta Jihar Borno.

Harin wanda ya fara da misalin karfe 1:35 na daren ranar Litinin, ya janyo arangama mai zafi tsakanin sojojin Najeriya da ƴan Boko Haram ɗin inda sojojin suka kashe da dama daga cikin su.

Rundunar sojin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X.

Rundunar ta kuma tabbatar da mutuwar sojoji biyu a yayin faɗan, yayin da sojojin suka ci gaba da bin sahun masu ƴan Boko Haram ɗin da suka tsere.

Garin Marte dai na daga cikin wuraren da Boko Haram ke yawan kai hari saboda matsayinsa na tasha da hanyar shiga garuruwa

Gwamnan Jihar, Babagana Umara Zulum, ya taba yin kira ga gwamnatin tarayya da ta ƙara azama wajen ƙarfafa ayyukan tsaro a garin Marte da kuma kare garin da komawa hannu ƴan Boko Haram.

Harin da aka kai na ranar Litinin ya sake tunatar da yadda Boko Haram ke ci gaba da zama barazana ga ƴan Najeriya.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp