Rundunar sojin kasar nan ta ce, sojojinta na Operation Hadin Kai sun yi nasarar daƙile wani hari da ‘yan Boko Haram da /ISWAP suka kai da tsakar dare a garin Marte ta Jihar Borno.
Harin wanda ya fara da misalin karfe 1:35 na daren ranar Litinin, ya janyo arangama mai zafi tsakanin sojojin Najeriya da ƴan Boko Haram ɗin inda sojojin suka kashe da dama daga cikin su.
Rundunar sojin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X.
Rundunar ta kuma tabbatar da mutuwar sojoji biyu a yayin faɗan, yayin da sojojin suka ci gaba da bin sahun masu ƴan Boko Haram ɗin da suka tsere.
Garin Marte dai na daga cikin wuraren da Boko Haram ke yawan kai hari saboda matsayinsa na tasha da hanyar shiga garuruwa
Gwamnan Jihar, Babagana Umara Zulum, ya taba yin kira ga gwamnatin tarayya da ta ƙara azama wajen ƙarfafa ayyukan tsaro a garin Marte da kuma kare garin da komawa hannu ƴan Boko Haram.
Harin da aka kai na ranar Litinin ya sake tunatar da yadda Boko Haram ke ci gaba da zama barazana ga ƴan Najeriya.