fidelitybank

Sojoji sun daƙile harin Boko Haram a Borno

Date:

Rundunar sojin kasar nan ta ce, sojojinta na Operation Hadin Kai sun yi nasarar daƙile wani hari da ‘yan Boko Haram da /ISWAP suka kai da tsakar dare a garin Marte ta Jihar Borno.

Harin wanda ya fara da misalin karfe 1:35 na daren ranar Litinin, ya janyo arangama mai zafi tsakanin sojojin Najeriya da ƴan Boko Haram ɗin inda sojojin suka kashe da dama daga cikin su.

Rundunar sojin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X.

Rundunar ta kuma tabbatar da mutuwar sojoji biyu a yayin faɗan, yayin da sojojin suka ci gaba da bin sahun masu ƴan Boko Haram ɗin da suka tsere.

Garin Marte dai na daga cikin wuraren da Boko Haram ke yawan kai hari saboda matsayinsa na tasha da hanyar shiga garuruwa

Gwamnan Jihar, Babagana Umara Zulum, ya taba yin kira ga gwamnatin tarayya da ta ƙara azama wajen ƙarfafa ayyukan tsaro a garin Marte da kuma kare garin da komawa hannu ƴan Boko Haram.

Harin da aka kai na ranar Litinin ya sake tunatar da yadda Boko Haram ke ci gaba da zama barazana ga ƴan Najeriya.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp