fidelitybank

Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ISWAP a Borno

Date:

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Multinational Joint Task Force (MNJTF) mai suna ‘Operation Hadin Kai, Sector 3’, sun dakile wani yunkurin kai hari da ‘yan ta’addar ISWAP suka yi a yankin Magumeri-Maiduguri a Borno.

Sojojin sun kuma kwato tarin alburusai daga hannun ‘yan ta’addan a wani farmaki da suka kai musu na dabara a yankin.

Lt.-Kol. Olaniyi Osaba, babban jami’in yada labarai na soji, MNJTF, N’djamena, Chadi, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Maiduguri.

Ya ce sojojin sun aiwatar da wani harin kwanton bauna, inda suka kawar da barazanar kafin ‘yan ta’adda su yi barna a kan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba.

Osaba ya ce sojojin sun ajiye kansu cikin dabara a kan hanyar ‘yan ta’addan inda suka yi ta artabu da su a lokacin da suka fito daga wani daji a kan babura.

“Da ganin sojojin, ‘yan ta’addan sun yi yunkurin guduwa amma sun ci karo da manyan bindigogi.

“Wannan gagarumin aiki ya tilasta musu barin makamansu da babura, wanda hakan ya kawo cikas ga shirinsu na tayar da rikici a yankin,” in ji shi.

Ya lissafta makaman da aka kwato sun hada da Bindigu AK-47 guda biyu, harsashi na musamman 7.62mm 51, mujallu guda biyu, harsashai 61 na 7.62 na NATO, buhunan tabar wiwi da Tramadol da dai sauransu.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...
X whatsapp