fidelitybank

Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ISWAP a Borno

Date:

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Multinational Joint Task Force (MNJTF) mai suna ‘Operation Hadin Kai, Sector 3’, sun dakile wani yunkurin kai hari da ‘yan ta’addar ISWAP suka yi a yankin Magumeri-Maiduguri a Borno.

Sojojin sun kuma kwato tarin alburusai daga hannun ‘yan ta’addan a wani farmaki da suka kai musu na dabara a yankin.

Lt.-Kol. Olaniyi Osaba, babban jami’in yada labarai na soji, MNJTF, N’djamena, Chadi, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Maiduguri.

Ya ce sojojin sun aiwatar da wani harin kwanton bauna, inda suka kawar da barazanar kafin ‘yan ta’adda su yi barna a kan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba.

Osaba ya ce sojojin sun ajiye kansu cikin dabara a kan hanyar ‘yan ta’addan inda suka yi ta artabu da su a lokacin da suka fito daga wani daji a kan babura.

“Da ganin sojojin, ‘yan ta’addan sun yi yunkurin guduwa amma sun ci karo da manyan bindigogi.

“Wannan gagarumin aiki ya tilasta musu barin makamansu da babura, wanda hakan ya kawo cikas ga shirinsu na tayar da rikici a yankin,” in ji shi.

Ya lissafta makaman da aka kwato sun hada da Bindigu AK-47 guda biyu, harsashi na musamman 7.62mm 51, mujallu guda biyu, harsashai 61 na 7.62 na NATO, buhunan tabar wiwi da Tramadol da dai sauransu.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp