fidelitybank

Sojoji sun ceto wasu mata ‘yan Boko Haram

Date:

Dakarun Sojojin Najeriya na Brigade 21 masu sulke a karamar hukumar Bama, sun ceto wasu ‘yan mata biyu da ‘yan ta’addan Boko Haram suka yi garkuwa da su a Sakandaren ’yan mata na gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno a shekarar 2014.

‘Yan matan biyu, Hannatu Musa da Kauna Luka, an ceto su ne a ranar Talata, 26 ga watan Yuli, shekaru takwas bayan sace su.

Kungiyar Boko Haram, ta yi garkuwa da dalibai mata 276, masu shekaru tsakanin 16 zuwa 18 a makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke garin Chibok a ranar 14 ga Afrilu, 2014.

A cewar wani rahoton sirri da aka samu daga manyan majiyoyin soji na Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a tafkin Chadi, ‘yan matan sun tsere daga sansanin Gazuwa, hedikwatar kungiyar Jama’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah. wa’l-Jihad, bangaren Boko Haram, wanda a da ake kira Gabchari, Mantari da Mallum Masari, da ke da nisan kilomita tara zuwa garin Bama.

Tun da farko dai, wasu ‘yan matan makarantar Chibok da aka ceto, Mary Dauda da Hauwa Joseph, sun shaida wa hukumomin soji cewa akwai ‘yan matan makarantar Chibok kusan 20 da har yanzu ake tsare da su kuma aka yi musu auren dole a sansanin Gazuwa.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp