fidelitybank

Sojoji sun ceto masu wasu masu yi wa kasa hidima a Katsina

Date:

Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana cewa, dakarun Brigade 17, na sojojin Najeriya tare da hadin gwiwar ‘yan sandan Najeriya, sun ceto wasu jami’an masu yiwa kasa hidima guda biyu da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a unguwar Yargoje da ke karamar hukumar Kankara a jihar Katsina.

Daraktan hulda da jama’a na rundunar, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Nwachukwu ya sanar da cewa, ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da jami’an hukumar ne a lokacin da suke kan hanyar wucewa daga Edo zuwa jihar Katsina, inda ya kara da cewa, daukin gaggawar da jami’an soji da ‘yan sanda suka yi ne ya yi nasarar kubutar da wadanda abin ya shafa daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su.

Ya ce an bai wa ‘yan kungiyar da aka ceto damar kula da lafiyarsu tare da tallafa musu domin tabbatar da lafiyarsu da ta jiki kuma a halin yanzu suna hannun ‘yan sandan Najeriya da ke Kankara.

Rundunar ta kuma nemi hadin kan jama’a da goyon bayan jama’a wajen samar da bayanan da suka dace don inganta ayyukan rundunar da suke yi na tunkarar wasu miyagun da ke barazana ga tsaron kasa.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp