fidelitybank

Sojoji sun ceto guda daga cikin matan Chibok

Date:

Sojoji sun yi nasarar ceto daya daga cikin ‘yan matan makarantar Chibok, wadda mayaƙan Boko Haram suka sace bayan shafe shekaru tara a hannunsu.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa an yi nasarar ceton ne a garin Maiduguri na jihar Borno, kuma an gabatar da ita a hedikwatar rundunar Operation Hadin Kai a ranar Litinin.

Dalibar, wadda ita ce ta hamsin da biyar a jerin ‘yan makarantan da aka sace, ta bayyana cewa mijinta na Boko Haram, ne ya taimaka mata wajen tserewa bayan miƙa wuya ga sojojin Najeriya.

Ta kuma shaida wa gidan talabijin din cewa ta haifi ƴaƴa biyu ga mijinta dan Boko Haram sai dai duk sun rasu.

Kwamandan sojojin, Manjo Janar Gold Chibuisi, ya bayyana cewa an miƙa ɗalibar a asibitin sojoji domin kula da lafiyarta, domin tabbatar da cewa tana cikin ƙoshin lafiya.

Ya ce za a miƙa ta ga gwamnatin jihar domin sada ta da iyalanta.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp