fidelitybank

Sojoji sun ceto direbobi daga hannun ISWAP a Borno

Date:

Dakarun Operation Hadin Kai, sun yi nasarar kubutar da wasu direbobin motocin wuta guda hudu da wasu da ake zargin ‘yan kungiyar IS ne a yankin yammacin Afirka (ISWAP) suka yi garkuwa da su.

An sace direbobin ne a ranar Asabar, 27 ga watan Mayu, kusa da kauyen Ngwom dake karamar hukumar Mafa. Mafa dai na da tazarar kilomita 50 daga gabas da Maiduguri babban birnin jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

Rahotanni sun bayyana cewa direbobin sun kai ’yan kwadago wadanda galibinsu masu yankan itace da lodi ne zuwa daji lokacin da ‘yan ta’adda dauke da makamai suka tare su.

‘Yan ta’addan sun tunkari direbobin ne da sunan cewa suna bukatar aikinsu domin kai mambobinsu wani kauye da ke kusa. Sai dai ba da jimawa ba ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da direbobin da fasinjojinsu.

Majiyar leken asirin ta bayyana cewa bayan samun wannan kiran na gaggawar, sojojin 112 Task Force Battalion, Mafa, tare da Civilian JTF da mafarauta sun tashi daga Mafa suka nufi kauyen Gullo domin neman wadanda aka sace a ranar 1 ga watan Yuni, 2023.

Majiyar ta ce da ganin sojojin da suke fada, ‘yan ta’addan sun yi watsi da wadanda harin ya rutsa da su, suka gudu yayin da sojoji suka yi musu zazzafar kora.

Dakarun fadan sun yi nasarar ceto mutanen hudu da aka yi garkuwa da su tare da kwato motocin.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp