fidelitybank

Sojoji sun ceto ƴan Chibok 3 bayan artabu da ƴan Boko Haram

Date:

Rundunar sojin hadin-gwiwa ta ‘operation Hadinkai’, ta ce, ta murkushe wasu ‘yan ta’adda 60, da kuma cafke mutum 120 da ake zargin ‘yan ta’adda ne a wani samame da suka kai a kauyukan jihar Borno.

Rundunar ta kuma ce, ta yi nasarar sake ceto wasu ‘yan matan Chibok uku da Boko Haram ta sace daga makarantar Sakandaren mata ta Chibok, a Borno tun 2014. In ji BBC.

Kwamandan rundunar, Manjo Janar Christopher Musa, da ke yi wa ‘yan jarida karin haske kan ayyukansu a hedikwatarsu da ke Maiduguri, ya ce jami’ansu na ci gaba da kokarin da katse duk wata hanya da mayaƙan ke samun taimako da makamai.

Sannan suna samun nasarar cafke mutanen da ke aiki da mayaƙan wajen kai musu abinci da sauran kayayyakin amfani.

‘Yan matan da aka ceto, tsakanin 27 ga watan Yuni zuwa 25 ga watan Yuli, sun hada da Ruth Bitrus, Karuna Luka da ke dauke da jariri sai kuma Hannatu Musa mai yara biyu.

A Afrilun shekara ta 2014 ne dai mayakan Boko Haram suka yi garkuwa da ‘yan mata 276 daga sakandaren kwana ta Chibok, galibinsu a wannan lokaci shekarunsu na tsakanin 16 zuwa 18.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp