Rundunar sojin hadin-gwiwa ta ‘operation Hadinkai’, ta ce, ta murkushe wasu ‘yan ta’adda 60, da kuma cafke mutum 120 da ake zargin ‘yan ta’adda ne a wani samame da suka kai a kauyukan jihar Borno.
Rundunar ta kuma ce, ta yi nasarar sake ceto wasu ‘yan matan Chibok uku da Boko Haram ta sace daga makarantar Sakandaren mata ta Chibok, a Borno tun 2014. In ji BBC.
Kwamandan rundunar, Manjo Janar Christopher Musa, da ke yi wa ‘yan jarida karin haske kan ayyukansu a hedikwatarsu da ke Maiduguri, ya ce jami’ansu na ci gaba da kokarin da katse duk wata hanya da mayaƙan ke samun taimako da makamai.
Sannan suna samun nasarar cafke mutanen da ke aiki da mayaƙan wajen kai musu abinci da sauran kayayyakin amfani.
‘Yan matan da aka ceto, tsakanin 27 ga watan Yuni zuwa 25 ga watan Yuli, sun hada da Ruth Bitrus, Karuna Luka da ke dauke da jariri sai kuma Hannatu Musa mai yara biyu.
A Afrilun shekara ta 2014 ne dai mayakan Boko Haram suka yi garkuwa da ‘yan mata 276 daga sakandaren kwana ta Chibok, galibinsu a wannan lokaci shekarunsu na tsakanin 16 zuwa 18.