Rundunar ‘yan sandan Operation Safe Haven (OPSH), ta bayyana cewa ta kama wasu mutane biyu kan kisan wani mai suna Naman Stephen Ngophe.
An kashe Ngophe ne a ranar 9 ga Satumba, 2023, a hannun wasu ‘yan bindiga da suka kai hari tare da kona gidan cocin Katolika da ke Kamanton a karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna.
Kakakin rundunar OPSH, Captain Oya James, wanda ya gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar OPSH, ya bayyana sunayensu da Ahmed Abdullahi da Hassan Mato.
Ya ce za a mika wadanda ake zargin ga ‘yan sanda da zarar an kammala bincike.
Sai dai Abdullahi ya musanta zargin, inda ya kara da cewa shi bai san da aikata laifin ba.
“Ina gida sai jami’an tsaro suka zo suka kama ni. An kawo ni nan aka hukunta ni mai tsanani ba tare da na aikata wani laifi ba. Ni daga gidan sarauta ne kuma ba zan iya yin irin wannan laifin ba. Ba a gaya mini abin da na yi ba sai yanzu.”