Dakarun Operation Safe Haven (OPSH) masu wanzar da zaman lafiya a Filato da wasu sassan jihohin Bauchi da Kaduna, sun kashe wasu da ake zargin ‘yan fashi ne guda hudu tare da cafke wasu 17 bisa laifuka daban-daban a yankunan da ke da alhakin gudanar da ayyukansu.
Jami’in yada labarai na rundunar Kyaftin James Oya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Jos.
Oya ya ce an kama wadanda ake zargin da laifin yin garkuwa da mutane, kisan kai, munanan hare-hare a kan al’umma, da safarar miyagun kwayoyi da dai sauransu.
Ya bayyana cewa, an kama wadanda ake zargin ne a wani samame na musamman da dakarunta suka gudanar tsakanin ranar 29 ga watan Oktoba zuwa 5 ga watan Nuwamba.
“Mun ceto hudu da aka yi garkuwa da su, mun hana yunkurin kai hari ga al’ummomi masu rauni kuma mun amsa kiraye-kirayen damuwa guda 13 a cikin lokacin da ake nazari,” in ji shi.
Oya ya ce kwamandan ta, Maj.-Gen. Abdusalam Abubakar ya godewa mazauna jihohin Filato, Bauchi, da Kaduna bisa goyon bayan sojoji da sauran jami’an tsaro a yunkurinsu na inganta tsaro a yankunansu.