An yi musayar wuta tsakanin dakarun Sojin Operation Thunder Strike/Whirl Punch da tsagerun ‘yan bindiga a yankin Labi, hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari.
Daily Trust ta rawaito cewa, akalla ‘yan bindiga 55 suka mutu a a rangar da a suka yi da sojoji kimamin su 75 da aka tirke kusa da makarantar Sojojin Najeriya NDA a Kaduna.
Daraktan yada labarai na shelkwatar tsaro, Manjo Janar Benard Onyeuko, ya bayyana hakan ranar Alhamis yayin hira da manema labarai.
Onyeuko ya yi bayanin cewa, yan bindigan sun sha ruwan wuta daga sama da kuma harsasan sojin kasa.
Ya ce: “Jami’an Sojin sama sun kai hari mabuyar yan bindga a kudancin Damari dake karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, bayan binciken kwakwaf. Harin Sojin saman ya hallaka ‘yan bindiga kusa da NDA, kuma sakamakon haka yan bindiga 55 sun mutu.”Â