Rundunar Operation Hadarin Daji ta samu nasarar kai hari mai zafi a kan sansani ‘yan bindiga da ke dajin Totsari da Kenkashi a karamar hukumar Tsafe cikin Jihar Zamfara.
Mazauna Mada ne suka sanar da manema labarai hakan a ranar Laraba, inda suka ce, lamarin ya auku ne yayin da sojojin suka kai samame kauyen Getawa, Unguwan Kade da kauyen Maigalma.
A cewar majiyar, yayin da ‘yan bindiga suka nemi tserewa daga sojoji, sun zubar da babura da shanu da suka sace, inda sojojin suka bisu suna ta harbin su.
Wani shaida da ya tabbatarwa da gidan talabijin na Channels ya ce, “Yayin da ‘yan bindigan suke kokarin tserewa daga rundunar sojojin sun bude musu wuta daga nan suka saki shanun satar suka fara gudu. Take anan sojojin suka bi su suna harbi. “Sakamakon samamen, an halaka dan ta’adda daya sannan an kwato babura da shanaye da dama da suka sace.”
“Sojojin sun bincike sansanin tsaf inda suka lalata shi sannan yanzu haka sun mamaye kauyakun suna ci gaba da bincike ko ina.”