fidelitybank

Sojoji sun bankaɗo lita 17,000 na ɗanyen man fetur da aka sace a Bayelsa

Date:

Rundunar Sojan Ruwa ta Najeriya, SOROH, ta kara kaimi wajen gudanar da aikin bincike a yankin Bayelsa.

Kwamandan NNS SOROH, Commodore Olushina Ojebode ne ya bayyana hakan a garin Diebu dake Kudancin Ijaw.

Sojoji sun gano tare da lalata kayayyakin da aka tace ba bisa ka’ida ba a cikin sintiri tsakanin 22 zuwa 29 ga watan Janairu.

Kwamandan ya ce an gano lita 17,000 na kayayyakin da ake zargin an samar da su daga cikin danyen mai da aka sace a wani gini da ke unguwar Diebu da ke karamar hukumar Ijaw ta Kudancin Bayelsa.

Kaftin Suleiman Abdulahi ya wakilce shi, ya bayyana cewa, aikin ya yi dai-dai da rundunar sojojin ruwan Najeriya ta Operation Delta Sanity, wanda aka kafa domin kawo karshen satar mai da kuma tudun mun tsira.

A cewarsa, aikin wanda ke da nufin yaki da satar danyen mai, tara mai ba bisa ka’ida ba, da sauran laifuffuka daban-daban a cikin muhallin ruwa na kasar, ya zuwa yanzu an samu nasarori, musamman a yankin na Sojan ruwan Najeriya SOROH.

Ya kara da cewa, tawagar sojojin ruwa da aka tura a tashar tsaro ta Naval (NNS 030) a lokacin da suke sintiri a yankin Zion na al’ummar Ezetu, a Kudancin Ijaw, sun gano man fetur da aka tace ba bisa ka’ida ba, kwatankwacin ganguna hudu ko kuma lita 1,200.

“Ci gaba da sintiri a cikin al’ummar Gbaran ya kai ga kama wani kwale-kwalen katako da ke jigilar buhu 275 na AGO da aka tace ba bisa ka’ida ba, kwatankwacin ganguna 55 ko kuma lita 16,500.

“Dukkan abubuwan da aka kwato an yi su ne da wasu tsare-tsare kan aikin satar danyen mai.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp