Hukumomi a kasar nan sun ce, jami’an tsaron ƙasar nan sun halaka ƴanbindiga 100 ciki har da gawurtaccen ɗanbindiga, Gwaska Dankarami a jihar Katsina.
Hadin gwiwar jami’an tsaron kasar ne suka ƙaddamar da harin a ranar Juma’a wanda ya yi sanadin kisan Gwaska Dankarami – wanda ya kasance mataimakin shugaban ƙungiya mai alaƙa da ISWAP.
Bayanai sun nuna cewa Gwaska Dankarami ya jima yana ɓuya a dajin Munumu da ke jihar Katsina.
Rahotonni sun ce sojojin sun lalata maɓoyar ƴanbindigar da dama a sassan jihar a lokacin harin, tare da ƙwato da kuma lalata wasu manyan bindigogi masu jigida da waɗanda aka ƙera a cikin gida.
Harin na zuwa ne bayan da a farkon mako ƴanbindigar suka yi garkuwa da mutum 43 mazauna ƙauyukan Maigora da ke yankin ƙaramar hukumar Dandume
Kwamishinan al’amuran cikin gida na jihar Katsina, Nasir Mu’azu ya bayyana matakin da wata gagarumar nasara a yaƙi da ƴanbindiga ake yi a jihar.
“Abin farin ciki ne ga jihar, domin wannan nasara ta taimaka wajen wargaza hadakar ƴanbindigar da ke addamar garuruwa da ƙauyukan yankunan ƙananan hukumomin Faskari da Kankara da Bakori da Malumfashi da kuma Kafur,” in ji Kwamishinan.
Ba dai wannan ne karon farko da jami’an tsaron Najeriya ke bayar da labarin kashe Gwaska Dankarami ba, ko a 2022 ma rundunar sojin sama ta ƙasar, ta yi iƙirarin kashe shi a irin wannan hari.