Majalisar dattijai ta yi kira ga sojojin Najeriya da su rinka kai hari kan ‘yan bindiga maimakon su jira sai an kai musu hari su nemi fansa.
Ta kuma nemi gwamnatin tarayya ta samar da jiragen yaki, domin fatattakar ‘yan ta’adda daga duka maboyarsu.
Wannan na cikin wasu abubuwa da aka cimma matsaya a kansu, bayan dogon lokacin da aka share a na muhawara kan tabarbarewar da tsaro.
A makon jiya, sai da ‘yan bindiga suka kashe 18 ciki har da wasu sojoji, tare da jikkata mutum 40, yayin da ‘yan ta’addan suka mamaye kauyen Galadima Kogo a karamar hukumar Shiroro a jihar Neja.