Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na kwanaki uku domin girmama sojoji 17 da suka rasa rayukansu a yayin wani harin da aka kai musu a Kwana Dutse, ƙaramar hukumar da ke jihar Neja.
Wannan zaman makoki zai gudana ne daga ranar 25 zuwa 27 ga watan Yuni, 2025, a matsayin alamar juyayi da girmamawa ga sojojin da suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare martabar ƙasa.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafinta na X, an umurci dukkan cibiyoyi da ma’aikatan soji a faÉ—in Ć™asar da su yi Ć™asa-Ć™sa da tutocin sojin Najeriya zuwa a wannan lokacin.
Rundunar ta ce wannan mataki na nuni ne da yadda ta ke ɗaukar rayuwar jami’anta da muhimmanci tare da nuna alhini ga iyalai da ƴan uwa na waɗanda suka mutu.
Rundunar Sojin Najeriya dai ta tabbatar da mutuwar sojojin ne sakamakon hare-haren da wasu Ć´an bindiga suka kai kan sansanonin soji da ke jahohin Neja da Kaduna.