fidelitybank

Sojoji na tauna Tsakuwa don Aya ta ji tsoro

Date:

A ranar Litinin ne runduna ta 3 ta sojojin Najeriya da ke Rukuba da ke kusa da Jos, ta fara atisayen harbe-harbe na shekara ta 2023 a rukunin kananan makamai da ke Miango a karamar hukumar Bassa ta jihar Filato.

Mukaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar Sojoji, Lt.-Col. Ishaku Takwa, ya bayyana a Jos cewa za a kammala atisayen ne a ranar 20 ga Afrilu.

“Bikin wani atisaye ne na shekara-shekara da ake shiryawa domin inganta kwarewar sojoji wajen amfani da makamai don inganta kwarewarsu ta kwararru.

“Zai hada da harba makaman soji daban-daban.

“An shawarci jama’a, musamman ma mutanen da ke zaune a kusa da babban yankin Miango da kada su firgita saboda ganin tarin sojoji da kuma jin karar harbe-harbe,” in ji shi.

Takwa ya gargadi mazauna yankin da su nisanci zango a duk tsawon lokacin da ake gudanar da atisayen. (NAN)

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp