Sojojin Isra’ila mata hudu da Hamas ta saki sun koma Isra’ila kamar yadda rundunar sojin kasar (IDF) ta tabbatar.
Sojojin hudu wadanda su ne Daniela Gilboa, da Liri Elbag, da Naama Levy da kuma Karina Ariev, za su kasance a cibiyar da aka tanadar ta musamman wajen ajiye wadanda aka saki kafin daga bisani su gana da iyayensu.
Tun da farko kafin sakin nasu mayakan Hamas sun taru a Dandalin Falasdinu da ke Gaza, domin danka wadanda za su saki ga kungiyar agaji ta Red Cross.
Wannan shi ne kashi na biyu na Isra’ilawa da Hamas ta yi garkuwa da su da ta saki bayan cimma yarjejeniyar dakatar da bude wuta tsakaninta da Isra’ila.
Ita ma Isra’ila za ta saka wa Hamas da sakin Falasdinawa wajen 200 da take rike da su a gidajen yarinta.
Ana sa ran Hamas za ta bayar da bayani a kan wasu Isra’ilawan 26 da za ta sake saki a makonnin da ke tafe.
Sojojin Isra’ila za su janye daga muhimman wurare a Gaza, domin Falasdinawa da suka yi gudun hijira su koma arewacin birnin.