fidelitybank

Sojoji ku tabbata kun fatattaki duk wanda ya hana Najeriya ruwa gudu – Tinubu

Date:

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bukaci shugabannin tsaron ƙasar da su tabbatar da ɗaura ɗamara domin magance matsalolin tsaron da ƙasar ke fuskanta.

Yayin da yake jawabi ga manyan hafsoshin tsaron a taron majalisar tsaron ƙasar da ya gudana a fadar gwamnatinsa ranar Juma’a da maraice, shugaban Tinubu, ya ce yayin da ake samun ci gaba a kakkabe matsalolin tsaro da ƙasar ke fama da su, akwai buƙatar ƙara jajircewa don tabbatar da magance matsalolin tsaron da ke ci wa ƙasar tuwo a ƙwarya.

“Nasarar da kuke samu abin a yaba ne. ‘Yan Najeriya na gani a ƙasa, amma ya kamata a yi ƙoƙarin kauce wa kura-kurai, irin wanda aka gani a baya-bayan nan a jihar Kaduna, haƙiƙa haɗin kai da ake samu takanin jami’an tsaro na ƙara inganta a watannin baya-bayan nan, amma a yanzu ba lokacin nuna murna ba ne, har sai mun kakkaɓe matsalar baki ɗayanta,” in ji shugaba Tinubu.

Shugaban ya kuma ya buƙaci sojojin da su tabbatar da muradin ƙasar na haƙo ganga miliyan biyu na man fetur a kowace rana a cikin rubu’in farko na shekarar 2024.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp