fidelitybank

Sojoji ku gaggauta kawo ƙarshen Ƴan Bindiga a Arewa

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya buƙaci dakarun ƙasar da ke yaƙi da ‘yan bindiga a yankin arewa maso yammacin ƙasar, su kawo ƙarshen matsalar nan ba da jimawa ba.

Ministan tsaron ƙasar Muhammad Badaru Abubakar ne ya bayyana haka lokacin wata ziyara da ya kai shalkwatar rundunar Operation Fansar Yamma mai yaƙi da ‘yan bindigar da ke jihar Zamfara.

Badaru ya ce ”shugaban ƙasa na matuƙar damuwa da matsalar rashin tsaro da jihar zamfara ke fuskanta, kuma ya umarci sojojin ƙasar su kawo ƙarshen matalar a yankin arewa maso yammacin ƙasar baki ɗaya”.

A lokacin ziyarar ministan ya yaba da irin tsare-tsaren sojojin da ke yaƙi da ‘yan bindigar tare da umartarsu su ci gaba da farautar manyan shugannin ‘yan bindigar yankin.

Ministan ya kuma ziyarci gidan gwamnatin jihar, inda ya tattauna da gwamnan jihar kan batutuwan da suka shafi tsaro a faɗin jihar.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp