Akalla sojoji biyu da dan sandan kwantar da tarzoma aka bayar da rahoton an kashe, bayan wani hari da ‘yan ta’addar kungiyar IS da ke Yammacin Afirka suka ka harii a wani sansanin soji a garin Molai na jihar Borno.
Al’ummar Molai na da tazarar kilomita 10 a kan titin Maiduguri zuwa Damboa, zuwa dajin Sambisa.
A cewar wata majiyar soji, ‘yan ta’addar sun kaddamar da harin ne a cikin manyan motocin yaki da dama. A cewar The Will.
Sai dai dakarun sojin Najeriya tare da na rundunar sojin sama na Operation Hadin Kai sun dakile hare-haren da aka kaddamar da Yammacin ranar Litinin da misalin karfe 6 na yamma, a kokarin da suke na fatattakar sojojin.
Sun yi artabu da sojoji na tsawon sa’a guda kafin daga bisani sojojin sama da na kasa su ka fatattaki maharan, inda aka tilasta musu ja da baya.