fidelitybank

Sojoji a Bama sun kama dan leken asirin Boko Haram

Date:

Dakarun runduna ta musamman ta 21 da ke Bama a jihar Borno, sun kama wani dan leken asiri na kungiyar ta’adda ta Boko Haram, Modu Babagana.

Politics Nigeria ta samu labarin cewa, Babagana ya tsere daga tsaren sojoji a Bama.
An fara kama dan ta’addan ne mai neman afuwar a watan Janairun 2020, saboda gudanar da ayyukan leken asiri kan sojoji a yankin Bama da Banki. Amma kwanaki kadan bayan an kai Babagana gidan yari, rahotanni sun ce, ya yi amfani da laya wajen saukaka tserewa daga gidan yari.

Daga bisani, hukumomi sun bayyana cewa ana neman sa.

A cikin makon nan ne aka sake kama shi tare da taimakon jami’an rundunar hadin gwiwa ta Civilian Task Force a babbar kasuwar garin Bama a lokacin da yake aikin sayan kayan aikin ‘yan ta’adda da makudan kudade.

A yayin gudanar da bincike na farko, wanda ake zargin ya amsa cewa, ya sa ido tare da bayyana inda sojojin suke da kuma motsin su ga mayakan na Boko Haram.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp