An harbe wata gogaggiyar ƴar jaridar Al Jazeera Shereen Abu Aqleh a yayin da take bayar da rahoto kan wani samame da dakarun sojin Isra’ila suka kai a birnin Jenin da ke Gaɓar Yammacin Kogin Jordan.
Kafar yaɗa labaran mai cibiya a ƙasar Qatar ta ce sojojin Isra’ila ne suka harbe ƴar jaridar mai shekara 51 “da gangan” kuma “ba tare da ta yi wani abu ba. Sannan an ji wa wani ɗan jaridar raunuka sakamakon harbinsa da aka yi.
Sai dai rundunar sojin Isra’ila ta ƙaryata cewa dakarunta kan ƴan jaridar suka kai hari.
Suna nuna yiwuwar “wataƙila ƴan bindigar Falasɗinu ne” suka kashe ta a yayin da ake musayar wuta.
Kafar yaɗa labaran mai cibiya a ƙasar Qatar ta ce sojojin Isra’ila ne suka harbe ƴar jaridar mai shekara 51 “da gangan” kuma “ba tare da ta yi wani abu ba. Sannan an ji wa wani ɗan jaridar raunuka sakamakon harbinsa da aka yi.