fidelitybank

Sojin Amurka ya cinna wa kansa wuta a gaban ofishin Isra’ila

Date:

Hukumomi a Washington sun ce wani soja ya cinna wa kansa wuta a gaban ginin ofishin jakadancin Isra’ila ranar Lahadi.

Mutumin wanda ba a tantance ba, an bayyana cewa yana cikin mawuyacin hali a asibiti.

Mai magana da yawun sojin Amurka ta tabbatar da faruwar lamarin.

Wakilin BBC ya ce wannan dai ba shi ne karon farko ba da hakan ke faruwa a bakin ofishin jakadancin Isra’ila ba a Amurka tun bayan É“arkewar yaÆ™i tsakanin Hamas da Isra’ilar.

Ko a watan Disambar bara wani ya aikata hakan a jihar Georgia.

Wani bidiyo ya É“ulla a shafukan sada zumunta inda a ciki aka ga mutum na ihu da cewa “A Æ´anta FalasÉ—inu” yayin da yake Æ™onewa, kamar yadda rahoton kafofin yaÉ—a labaran Amurka ya ce.

An tura jami’an sashen kwance bom zuwa wurin kan fargabar da aka yi game da wata mota da ake iya alaÆ™antawa da mutumin.

Daga bisani an bayyana cewa ba a gano wasu abubuwan hadari ba a cikin motar.

Ba a sami wani ma’aikacin ofishin jakadanci ba da ya ji rauni, kamar yadda mai magana da yawun ofishin jakadancin ta shaida wa jaridar New York Times.

Cikin wata sanarwa, ma’aikatar harkokin wajen Isra’ila ta ce ma’aikatan ofishin jakadancin ba su san mutumin ba.

Ƴan sanda sun ce mutumin ya yi amfani da fetur sannan an ga tutar Falasɗin a wajen da lamarin ya faru.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp