fidelitybank

Soji sun daƙile harin mayaƙan ISWAP a Borno

Date:

Rundunar Operation Hadin Kai wadda ke ƙarƙashin sojin Najeriya ta daƙile wani yunƙuri na harin kwanton ɓauna kan wasu motoci a kan hanyar Bama da ke Jihar Borno.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewa, mayaƙan ISWAP ne suka buɗe wuta a manyan hanyoyin Jihar Borno biyu. Rahotanni sun ce, tun da farko mayaƙan sun saka shingaye da dama a kwanar garin Banki, domin garkuwa da fararen hula a Ƙaramar Hukumar Bama a ranar Asabar.

Wani babban kwamanda ya shaida cewa, dakarun da ke shawagi domin tabbatar da tsaro a yankin ne suka daƙile hare-haren masu iƙirarin jihadin jim kaɗan bayan an kira su a waya an shaida musu halin da ake ciki.

Kwamandan ya bayyana cewa, mayaƙan ISWAP ɗin waɗanda suke riƙe da wasu matafiya a kan hanya, sun gudu bayan ganin sojojin, inda suka bar waɗanda suka kama.

Ya bayyana cewa, harbin bindiga da mayaƙan suka yi, ya yi sanadin fashewar gilasan baya na motocin matafiyan, amma babu wanda ya rasu.

A ɗayan ɓangaren kuma, dakarun bataliya ta 152 a yayin da suke shawagi a kan hanyar Bula Yobe – Darel Jamel a ranar dai ta Asabar sun daƙile wani harin mayaƙan na ISWAP.

Haka kuma sojojin bakwai ne, suka tsallake rijiya da baya a sakamakon nakiya da ƴan ISWAP suka dasa musu a hanyar Damboa zuwa Maiduguri.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp