fidelitybank

Soji sun daƙile harin mayaƙan ISWAP a Borno

Date:

Rundunar Operation Hadin Kai wadda ke ƙarƙashin sojin Najeriya ta daƙile wani yunƙuri na harin kwanton ɓauna kan wasu motoci a kan hanyar Bama da ke Jihar Borno.

Jaridar PRNigeria ta rawaito cewa, mayaƙan ISWAP ne suka buɗe wuta a manyan hanyoyin Jihar Borno biyu. Rahotanni sun ce, tun da farko mayaƙan sun saka shingaye da dama a kwanar garin Banki, domin garkuwa da fararen hula a Ƙaramar Hukumar Bama a ranar Asabar.

Wani babban kwamanda ya shaida cewa, dakarun da ke shawagi domin tabbatar da tsaro a yankin ne suka daƙile hare-haren masu iƙirarin jihadin jim kaɗan bayan an kira su a waya an shaida musu halin da ake ciki.

Kwamandan ya bayyana cewa, mayaƙan ISWAP ɗin waɗanda suke riƙe da wasu matafiya a kan hanya, sun gudu bayan ganin sojojin, inda suka bar waɗanda suka kama.

Ya bayyana cewa, harbin bindiga da mayaƙan suka yi, ya yi sanadin fashewar gilasan baya na motocin matafiyan, amma babu wanda ya rasu.

A ɗayan ɓangaren kuma, dakarun bataliya ta 152 a yayin da suke shawagi a kan hanyar Bula Yobe – Darel Jamel a ranar dai ta Asabar sun daƙile wani harin mayaƙan na ISWAP.

Haka kuma sojojin bakwai ne, suka tsallake rijiya da baya a sakamakon nakiya da ƴan ISWAP suka dasa musu a hanyar Damboa zuwa Maiduguri.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp