fidelitybank

Sojan Najeriya ya kashe kansa bayan an gano ɗan ƙungiyar ISWAP ne

Date:

Rahotanni daga yankin Arewa maso Gabashin na cewa wani sojan kasa, ya kashe kansa bayan da aka kama shi bisa tuhumar cewa, yana aiki tare da mayaka masu ikirari jihadi na kungiyar ISWAP.

Wakilin BBC ya ce wata majiya mai kusanci da rundunar sojojin Najeriya ta sanar da shi cewa, lallai sojan na da hannu a wasu hare-hare da aka kai kan wasu al’umomin jihar Yobe a cikin makonni da suka gabata.

Manyan hafsoshin sojin kasa sun fara sa ido kan sojan ne bayan da aka kai wasu hare-hare biyu a garuruwan Geidam da Gashua na jihar ta Yobe, kuma daga nan suka fara bibiyar wuraren da yake zuwa cikin sirri.

An kuma kama shi yayin da yake kokarin tserewa, bayan da ya gane cewa dubunsa ta cika.

Sai dai sojan wanda kwararre ne wajen sarrafa makamai, ya kwace wata bindiga a hannun daya daga cikin sojojin da ke rakiyarsa, kuma ya kashe kansa duk da cewa, an saka masa ankwa a hannu.

A makon jiya wasu wadanda ake kyautata zaton mayakan ISWAP ne suka kai wani hari kuma suka kashe akalla mutum goma, ciki har da mata.

Wannan harin ya biyo bayan wani harin na daban da aka dasa wani bam wanda ya halaka mutum shida, baya ga raunata wasu mutum 19 a jihar Taraba, harin da kungiyar ISWAP ta dauki alhakin kai shi.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...
X whatsapp