fidelitybank

Siyasar Kano: Kwankwaso ya aurar da diyar Shekarau

Date:

Daurin auren diyar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau ya hada ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban a taron da a ka gudanar a ranar Juma’a.

A wajen taron, wanda mutane da yawa ke ganin tamkar nuna siyasa ce ba tare da dacin rai ba, tsohon gwamna, Musa Rabiu Kwankwaso ya zama Waliyyi, wanda ya baiwa Adamu Yusuf Maitama ‘yar Shekarau.

PlatinumPost ta rawaito cewa, Kwankwaso ya na da karfi a jam’iyyar adawa ta PDP yayin da Shekarau ke zaman Sanata a jam’iyyar APC mai mulki.

Daurin auren wanda ya gudana a masallacin Umar Bn Khattab da ke kan titin Zaria, ya samu halartar shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan da Sanata Barau Jibrin da dai sauransu.

Daruruwan magoya bayan manyan jam’iyyun siyasar jihar guda biyu ne su ka halarci daurin auren, kowannensu kuma na rera wakokin goyon bayan shugabanninsa, musamman ma ‘yan Kwankwasiyya da alamar jar hula ta mamaye wurin.

Yayin da Kwankwaso ya zarce gidansa bayan an daura auren, shi kuwa Shekarau ya kai shugaban majalisar dattawa zuwa gidansa, daga bisani kuma ya raka shi, domin ta’aziyyar Kwankwaso bisa rasuwar kaninsa.

A baya Shekarau ya ziyarci gidan Kwankwaso, a ranar Alhamis, domin yin ta’aziyya.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp