fidelitybank

Siyasar Kano: Kwankwaso ya aurar da diyar Shekarau

Date:

Daurin auren diyar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Ibrahim Shekarau ya hada ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban a taron da a ka gudanar a ranar Juma’a.

A wajen taron, wanda mutane da yawa ke ganin tamkar nuna siyasa ce ba tare da dacin rai ba, tsohon gwamna, Musa Rabiu Kwankwaso ya zama Waliyyi, wanda ya baiwa Adamu Yusuf Maitama ‘yar Shekarau.

PlatinumPost ta rawaito cewa, Kwankwaso ya na da karfi a jam’iyyar adawa ta PDP yayin da Shekarau ke zaman Sanata a jam’iyyar APC mai mulki.

Daurin auren wanda ya gudana a masallacin Umar Bn Khattab da ke kan titin Zaria, ya samu halartar shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan da Sanata Barau Jibrin da dai sauransu.

Daruruwan magoya bayan manyan jam’iyyun siyasar jihar guda biyu ne su ka halarci daurin auren, kowannensu kuma na rera wakokin goyon bayan shugabanninsa, musamman ma ‘yan Kwankwasiyya da alamar jar hula ta mamaye wurin.

Yayin da Kwankwaso ya zarce gidansa bayan an daura auren, shi kuwa Shekarau ya kai shugaban majalisar dattawa zuwa gidansa, daga bisani kuma ya raka shi, domin ta’aziyyar Kwankwaso bisa rasuwar kaninsa.

A baya Shekarau ya ziyarci gidan Kwankwaso, a ranar Alhamis, domin yin ta’aziyya.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp